Luke 19

1Yesu ya shiga Yariko ya na wucewa cikinta. 2Sai ga wani mutum a wurin mai suna Zakka. Shugaba ne na masu karban haraji, kuma mai arziki ne.

3Yana kokarin ya ga ko wanene Yesu, amma bai iya gani ba sabo da yawan jama’a, domin shi gajere ne. 4Sai ya ruga gaba ya hau itacen baure domin ya gan shi, saboda Yesu zai wuce ta wannan hanya.

5Sa’adda Yesu ya zo wurin, ya kalli sama sai ya ce masa, “Zakka, ka sauko da sauri, domin yau dole in sauka a gidanka.” 6Sai ya sauko da sauri, ya karbe shi da farin ciki. 7Sa’adda dukansu suka ga wannan, sai suka yi gunaguni, cewa, “Ya ziyarci mutum mai zunubi.”

8Zakka ya tsaya ya ce wa Ubangiji, “Duba, Ubangiji, zan ba matalauta rabin arzikina, idan kuma na cuci wani a kome, zan mai da adadinsa sau hudu.” 9Yesu ya ce masa, “Yau ceto ya shigo wannan gida, domin shi ma dan Ibrahim ne. 10Gama Dan Mutum ya zo ne domin ya nemi, ya kuma ceci batattun mutane.”

11Da suka ji wadannan abubuwan, ya cigaba da magana, sannan ya fada masu wani misali, domin yana kusa da Urushalima, sai suka yi tsamani mulkin Allah za ya bayyana nan da nan. 12Sai ya ce, “Akwai wani mutum mai sarauta wanda ya tafi wata kasa mai nisa domin ya karba wa kansa mulki sa’annan ya dawo.

13Sai ya kira bayinsa guda goma, ya ba su fam goma, sai ya ce masu, ‘Ku yi kasuwanci da wannan har sai na dawo.’ 14Amma mutanensa suka ki shi sai suka aiki jakadu bayansa, cewa, ‘Ba za mu yarda wannan mutum ya yi mulki a kanmu ba.’ 15Anan nan sa’adda ya koma kuma, bayan da ya sami mulkin, sai ya ba da umarni a kira masa bayin da ya basu kudi, domin ya san ribar da suka samu wajen kasuwancin da suka yi.

16Na farkon ya zo wurinsa, cewa, ‘Ubangiji, fam nan na ka ya yi riban fam goma.’ 17Masaraucin ya ce masa, ‘Madalla, bawan kirki. Domin ka yi aminci a karamin abu, za a baka iko kan birane goma.’

18Na biyun ya zo, yana cewa, ‘Fam na ka, Ubangiji, ya yi ribar fam biyar.’ 19Sai masarauncin yace masa, ‘Ka dauki mulkin birane biyar.’

20Wani kuma ya zo, yana cewa, ‘Ubangiji, ga fam naka da na ajjiye shi da kyau cikin kaya, 21gama na ji tsoronka, domin kai mutum mai tsanani ne. Kana daukar abu da baka ajiye ba, kana kuma girbin abin da ba ka shuka ba.’

22Masarauncin ya ce masa, ‘Da kalmominka zan shari’antaka, kai mugun bawa. Ka sani cewa ni mutum mai tsanani ne, ina daukan abinda ban ajiye ba, ina kuma girbin abinda ban shuka ba. 23To don me ba ka kai kudi na wurin masu banki ba, saboda bayan da na dawo zan karbe shi da riba?’

24Masaraucin ya ce wa wadanda suke a tsaye a wurin, ‘Ku karba fam da ke a wurinsa, ku ba mai fam goman nan.’ 25Suka ce masa, ‘Ubangiji, yana da fam goma.’

26‘Ina ce maku, duk wanda yake da abu za a kara masa, amma wadda bai da shi, za a karba sauran da ke wurinsa. 27Amma wadannan abokan gabana, wadanda ba sa so in yi mulki bisansu, a kawo su nan a kashe su a gaba na.’

28Da ya fadi wadannan abubuwan, sai ya yi gaba, yana tafiya zuwa Urushalima.

29Ananan sa’adda ya zo kusa da Baitfaji da Baitanya, a kan tudu da a ke kira Zaitun, sai ya aiki almajiransa guda biyu, cewa, 30cewa, “Ku tafi cikin kauye da ke gabanku. Sa’adda ku ka shiga, za ku same dan aholaki da ba a taba hawansa ba. Ku kwance sai ku kawo mani shi. 31Idan wani ya tambaye ku, ‘Don me ku ke kwance shi?’ Ku ce, ‘Ubangiji ne ke bukatarsa.”

32Wadanda aka aike su suka je sun sami aholakin kamar yadda Yesu ya gaya masu. 33Sa’adda suna kwance aholakin, sai masu shi suka ce masu, “Don me ku ke kwance aholakin?” 34Suka ce, “Ubangiji yana bukatar sa.” 35Suka kawo wa Yesu, suka shimfida tufafinsu akan aholakin sai suka dora Yesu akansa. 36Da yana cikin tafiya, suka shimfida tufafinsu akan hanya.

37Da ya yi kusa da gangaren tudun Zaitun, sai dukan taron almajiransa suka fara yin murna suna kuma yabon Allah da murya mai karfi domin dukan ayukan al’ajibi da suka gani, 38cewa, “Albarka ta tabbata ga sarki da ke zuwa cikin sunan Uba! Salama a sama da daraja mafi daukaka kuma!”

39Wadansu Farisawa daga cikin taron jama’a suka ce masa, “Malam, ka tsauta wa almajiranka.” 40Yesu ya amsa ya ce, “Ina gaya maku gaskiya, in wadannan sun yi shiru, duwatsu za su yi shewa.”

41Sa’adda Yesu yana kusatowa, sai ya yi kuka akan birnin, 42cewa, “Da kun san wannan rana, ko ku ma, abubuwan da ke kawo maku salama! Amma yanzu an boye su daga idanunku.

43Gama rana zata ta zo a gareki, da makiyan ki zasu gina ganuwa a kewaye da ke, su kuma fada maki daga kowace gefe. 44Za su sare ki kasa tare da ‘ya’yanki. Ba za su bar wani dutse akan dan’uwansa ba, domin ba ki lura da lokacin da Allah ya na kokarin ceton ki ba.”

45Yesu ya shiga Haikalin sai ya fara korar masu sayarwa, 46ya na ce masu, “A rubuce yake, ‘Gida na zai zama wurin addu‘a,’ amma kun mayar da shi kogon mafasa.”

47Yesu yana nan yana koyarwa kowace rana a cikin haikali. Amma manyan firistoci da marubuta da shugabanin jama’a suna so su kashe shi, amma ba su sami hanyar yin wannan ba, domin mutane suna sauraron sa sosai.

48

Copyright information for HauULB